Sunday, August 10, 2014

MA'ANAR KALMAR SHAHADA (1)

Shahadu biyu sune: Shaidawa babu abin bautawa da gaskiya sai Allah, da shaidawa lallai Annabi Muhammadu (S.A.W) Manzon Allah ne. Kuma sune tushen addinin Musulunci kuma gimshiqinsa na farko, wanda dashine bawa ke shiga Addinin Musulunci, saboda haka, duk wanda bai shaida da waxannan shahadu biyuba, to shi ba Musulmi bane Abdullahi xan Umar (Allah Ya qara musu yarda) ya ruwaito daga Annabi (S.A.W) cewa yace: "An gina musuluncine akan (gimshiqai) biyar, shaidawa babu abin bautawa da gaskiya sai Allah kuma Annabi Muhammadu Manzon Allah ne, da tsaida sallah, da bada zakka, da aikin hajji, da azumtan watan ramadana." Bukhari da Muslim ne suka ruwaitoshi. Saboda haka, abu nafarko daya wajaba ga bawa ya fara sani acikin addinin Musulunci shine; gimshiqinsa na farko, wato ya san ma'anar Kalmar shahada da hukunce hukuncenta. Kuma Yayinda Annabi (S.A.W) ya aika Mu'azu xan Jabal zuwa (qasar) Yaman amatsayin mai kira (zuwa ga Allah) kuma malami yace masa: "Lallai zaka tafine zuwaga wasu jama'a daga ma'abuta littafi, saboda haka kafarada kiransu zuwaga shaidawa babu abin bautawa da gaskiya sai Allah, kuma lallai ni (Muhammadu) manzon Allah ne, idan sukayi biyayya akan haka, sai ka sanardasu cewa Allah Ya farlanta salloli biyar akansu cikin kowane yini da dare…" zuwa qarshen hadisin. Imamu Muslimne ya ruwaitoshi daga hadisin Abdullahi xan Abbas Hakananma Imamul Bukhari ya ruwaito shi da lafazin; " Abu na farko da zaka kirasu zuwa gareshi ya kasance shine su kaxaita Allah. Kuma bayanin wannan ya zo acikin hadisin (da akafi sani da hadisin) Jibril mai tsayinnan wanda (Jibrilu)ya tambayi Annabi (S.A.W) gameda martabobin addinin Musulunci; Imani, Musulunci da Ihisani, sannan sai Annabi (S.A.W) yace wa sahabbansa- kamar yadda yazo aqarshen hadisin: "Wannan Jibirilune yataho gareku don ya karantar daku addininku". Saboda haka, abubuwa nafarko da suka wajaba asani cikin al'amuran addini, sune abubuwanda hadisin Jibrilu yake kunshe dasu, kuma martaba tafarko daga martabobin addini, itace martabar Musulunci, a musulunci kuwa rukuni na farko daga cikin rukunnansa shine shaidawa babu abin bautawa da gaskiya sai Allah kuma lallai Annabi Muhammadu (S.A.W) manzon Allahne.

No comments:

Post a Comment