Wednesday, March 11, 2015

ALHAJRUL-ASWAD (DUTSE MAI ALBARKA)

Hadisi ya tabbata cewa wannan dutse daga cikin Aljannah yake, kuma lokacin da aka saukar dashi fari ne, kal, yawan sabon mutane yasa ya zama, baki, wannan dutse, yasha gwagwarmaya iri-iri, a tsawon tarihi, lokacin da kuraishawa zasu sabinta ginin kaabah, lokacin Manzon Allah saw, yana da shekara talatin da bakwai, sunyi sabani, gamai da wanda zai dora wannan dutse. karshe, suka amince sa cewa, duk wanda ya fara shigowa, shine zaiyi hukunci, kuma zasu yarda da hukuncinsa, sai Manzon Allah saw ya fara shigowa, kuma dukkansu, sukayi farin ciki, da zuwansa, saboda sun sanshi, da gaskiya, da Amana, da Adalci, sai ya nemi, su nada wakilai daga ko wacce kabila, ya shinfida, mayafinsa, ya dora dutsan akai, yace ko wane wakili ya kama gefe, daya, su daga tare, sukai wajan, shi kuma ya daidaita shi, , Manzon Allah saw yace, wannan dutsan zaizo ranar a kiyama da ido da harshe zaiyi sheda ga duk ya sunbace shi, wannan dutse yana da sunnoni guda biyar 1- Ashafe shi da hannu, ya sunbace shi, yayi kabbara 2-Idan ba hali sai ya tabashi, ya sunbaci hannunsa 3- Idan ba hali, sai ya tabashi da sandarsa sai ya sunbaci inda ya taba da sandar. 4- Idan haka bata samu ba, sai ya nuna shi da hannu, yayi kabbara, ba tare da ya saunbaci hannunba. 5- Idan babu cunkoso, yana iya yin sujjada akansa.

No comments:

Post a Comment