Hakika Sallah tana da matsayi
mai girma a cikin Addinin
Musulunci, babu wata Ibada
da takai Sallah, domin ita ce
ginshikin Addini, Sallah ita ce
farkon farilla da Allah ya
farlanta ma bayinsa bayan
(Tauhidi) watau kadaita
Allah.
Sallah ita ce farkon abin da
za’a fara yiwa bawa
hisabi akansa cikin dukkan
ayyukansa ranar Kiyama,
kamar yadda ya zo a Hadisin
Annabi (Sallallahu Alaihi
Wasallam) da yake cewa:
“Farkon abin da za’a fara
yiwa bawa hisabi akansa
ranar Kiyama shi ne Sallah, in
tayi kyau dukkan sauran aiki
sun yi kyau, in ko bata yi
kyau ba to dukkan sauran aiki
sun baci.
A wani Hadisin
kuma Manzon Allah
(Sallallahu Alaihi Wasallam)
yana
mana gargadi akan kula da
Sallah, sai ya rika cewa: “Ku
kula da Sallah, kuma ku kula
da abin da kuka mallaka
watau (bayi)”.
Hakika an wajabta ma
Musulmi Sallah
koda ya kasance a fagen yaki
ne ba a yardar masa
yabar Sallah ba.
Saboda fadar Allah
madaukakin sarki
“Ku kiyaye da Sallah, da kuma
Sallah ta tsakiya, ku
tsaya saboda Allah, kuna masu
bin Allah”.
Allah (Subhanahu Wata’ala)
ya yi alkawarin cewa zai yi
ma wadanda suke tozartar da
Sallah azaba mai tsanani
sai ya ce:
“Sai aka samu wasu da suka
maye musu, suka
rika tozartar da Sallah sukla bi
sha’awar duniya, da
sannu zasu cimma hasara”.
No comments:
Post a Comment