Rukunan Imani su ne: Imani da Allah da Mala'ikunSa da LittafanSa da ManzanninSa da Ranar Lahira da kaddara; alherinta da sharrinta.
Allah Madaukakin Sarki ya ce:
Ma'ana: ((Sai dai (mai) biyayya (ga Allah shi ne) wanda ya yi imani da Allah da Ranar Lahira da Mala'iku da Littafai da Annabawa)). (Bakara: 177)
Haka nan Allah Madaukaki ya ce:
Ma'ana: ((Manzo ya yi imani da abin da aka saukar masa daga Ubangijinsa haka nan Muminai; kowa -daga cikinsu- ya yi imani da Allah da Mala'ikunSa da LittattafanSa da ManzanninSa, (suna cewa) "Mu ba ma banbanta tsakanin manzannin naSa, kuma suka ce: "mun ji mun bi, ka gafarta mana ya Ubangijinmu, kuma gare ka ne makoma take"). (Bakara: 285)
Allah Madaukaki yace:
Ma'ana: ((Hakika Mu, kowanne abu mun halicce shi ne da wani tsari)). (kamar: 49)
Annabi (s.a.w) ya ce:
Ma'ana: "Imani shi ne ka yarda da Allah da Mala'ikunSa da LittattafanSa da ManzanninSa da Ranar Lahira, kuma ka yarda da kaddara; alherinta da sharrinta".
No comments:
Post a Comment