Tuesday, February 10, 2015

IMANI DA TAURARI SHIRKA CE

IMANI DA TAURARI SHIRKA CE Zaidu xan khalidu al-juhani ya riwaito cewa:“Wata rana a Hudabiyya, Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama ya ba mu sallar safe, bayan an xauke ruwan sama, da aka kwana ana yi. Da ya qare sallar ya juyo ya fuskance mu. Sai ya ce: ko kun ji abin da Unbangijinku ke faxa? Muka ce: Allah da Manzonsa kaxai ke da sani.Daga nan sai ya ce:“Allah Ya ce ne: Wayewar garin nan wani bawa nawa ya yi imani da ni, wani kuma ya kafirce mani. Duk wanda ya ce:“Ruwan nan Allah ne Ya shayar da mu a cikin ikonsa da rahamarsa”.To shi ne wanda ya yi imani da ni, ya kafirce ma taurari. Shi kuwa wanda ya kafirce mani ya kuma yi imani da taurari shi ne wanda ya ce: “Tauraruwa kaza da kaza ne suka shayar da mu wannan ruwa (Buhari: 2/333). Haka kuma duk wanda ya karanta jadawalin abubuwan da za su faru na gaibi wanda ake kirdado dabra da kaiwa da komowar taurari, a cikin wata jarida ko mujalla, ya kuma yi imani da abin to, babu shakka shi ma mushriki ne. Savanin wanda karantawa kawai ya yi don nishaxi. Shi mai laifi ne kawai. Dalili kuwa shi ne, ba abu ne yardadde a shari'a ba, mutum ya nemi samun wani nishaxi ta hanyar karanta wasu abubuwa da suka qunshi Shirka. Domin shexan na iya amfani da wannan dama ya tuqa masa tuwon tulu, a wayi gari ya faxa cikin mushrikai.

No comments:

Post a Comment