Rukunan Imani su ne: Imani da Allah da Mala'ikunSa da LittafanSa da ManzanninSa da Ranar Lahira da kaddara; alherinta da sharrinta.
Allah Madaukakin Sarki ya ce:
Ma'ana: ((Sai dai (mai) biyayya (ga Allah shi ne) wanda ya yi imani da Allah da Ranar Lahira da Mala'iku da Littafai da Annabawa)). (Bakara: 177)
Haka nan Allah Madaukaki ya ce:
Ma'ana: ((Manzo ya yi imani da abin da aka saukar masa daga Ubangijinsa haka nan Muminai; kowa -daga cikinsu- ya yi imani da Allah da Mala'ikunSa da LittattafanSa da ManzanninSa, (suna cewa) "Mu ba ma banbanta tsakanin manzannin naSa, kuma suka ce: "mun ji mun bi, ka gafarta mana ya Ubangijinmu, kuma gare ka ne makoma take"). (Bakara: 285)
Allah Madaukaki yace:
Ma'ana: ((Hakika Mu, kowanne abu mun halicce shi ne da wani tsari)). (kamar: 49)
Annabi (s.a.w) ya ce:
Ma'ana: "Imani shi ne ka yarda da Allah da Mala'ikunSa da LittattafanSa da ManzanninSa da Ranar Lahira, kuma ka yarda da kaddara; alherinta da sharrinta".
A'UZUBILLAHI MINASH SHAIDANIR RAJIM
BISIMILLAHIR RAHAMANIR RAHIM.
ALHAMDULILLAHI RABBIL ALAMIN
WASSALATU WASSALAMU ALAL MABA'USI RAHAMATAN LIL ALAMIN NABIYYUNA MUHAMMADIN WA'ALA ALIHI WA AS'HABIHI WAMAN TABI'AHUM BI'IHSANIN ILA YAUMIDDIN.®®®
No comments:
Post a Comment